Name:muslim👳♂️❤️
Father's name:Adam❤️👳♂️
Ideal:Muhammad (PBUH)❤️
Holy book:Qur'an📖💚
Religion :Islam💦
Present adress:Duniya 😊
لا إله إلا الله محمد رسول💫
Arewa fam, let’s connect before you go to work.
Drop your X username below Let’s promote your account and get followed. ⬇️ Like and Retweet for more mutuals.
$TAO
so many people are afraid of getting their ideas stolen.
but if you have good ideas, you should get used to people stealing them. that's the best validation you can get.
if it's not worth stealing, then it's not worth building. and if your idea gets anywhere, then the next phase of your growth will be a result of you doing it in a way that is so uniquely you, that people stealing it can't hurt you - it can only help you.
Ladubban Hira da Mutane
1- Ka guji ƙarya, da gulma, da yi da mutane, da yi musu tonon silili.
2- Yawaita amfani da kalmomin kyautata zance: "Don Allah", "in ba damuwa", "na gode", "madalla!"
3- Kada ka shagaltar da abokan hirarka da yawan faɗa musu matsalolinka. Ka zama mai yakana.
4- Kada ka riƙa tambayar abokin hirarka keɓantattun abubuwa da suka shafi rayuwarsa.
5- Idan wani yana ba da labarin da ka sani, kada ka katse hanzarinsa, bari ya kai gaci, kana mai nuna labarin ya shige ka.
6- Kada ka wawantar da ra'ayin wasu, ka wulakanta su.
7- Kada ka nuna ra'ayinka shi ne ƙololuwar gaskiya. Ka riƙa cewa: A ganina.
8- Ka riƙa rarraba dubanka ga waɗanda kake zantarwa, kada ka sa mutum ɗaya a gaba kana yi masa kallon ƙurilla.
9- Ka guji gamammen hukunci a kan mutane, kamar ka ce "Duk mutane sun lalace.."
10- Kada ka ce wa mai zance: "ƙarya kake" haka gatsal. Ka koyi cewa: Ni kuma na ji an ce kaza ne ya faru.
* Umar bn Khattab (RA) ya ce: "Idan aka wurgo kalmar da za ta ɓata maka rai, ka sunkuya ta wuce ta samanka."
* An tambayi Abbasu ɗan AbdulMuɗɗalibi (RA): Da kai da Manzon Allah (SAW) wane ne babba?
Ya ce: "Shi ne babba, amma an haife ni kafin haihuwarsa."
* Aɗa'u ɗan Abu Rabahi ya ce: Mutum yakan zantar da ni wani labari, sai in nutsu, ina sauraronsa, duk da tun kafin a haife shi, na san wannan labarin da yake gaya mini."
* Ma'amunu ya tambayi sunan wani mutum da ake kira: Sayyid ɗan Anas, ya ce: "Kai ne Sayyid?"
Mutumin ya ce: "A'a, Sarkin muminai shi ne sayyid (shugaba), ni ɗan Anas nake."
Dr. Aminu Ismail